1
Luka 12:40
Sabon Rai Don Kowa 2020
Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Compara
Explorar Luka 12:40
2
Luka 12:31
Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
Explorar Luka 12:31
3
Luka 12:15
Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
Explorar Luka 12:15
4
Luka 12:34
Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
Explorar Luka 12:34
5
Luka 12:25
Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
Explorar Luka 12:25
6
Luka 12:22
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
Explorar Luka 12:22
7
Luka 12:7
Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
Explorar Luka 12:7
8
Luka 12:32
“Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
Explorar Luka 12:32
9
Luka 12:24
Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Explorar Luka 12:24
10
Luka 12:29
Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
Explorar Luka 12:29
11
Luka 12:28
In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
Explorar Luka 12:28
12
Luka 12:2
Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
Explorar Luka 12:2
Inici
La Bíblia
Plans
Vídeos