1
Yah 1:12
Littafi Mai Tsarki
Amma duk iyakar waɗanda suka karɓe shi, wato, masu gaskatawa da sunansa, ya ba su ikon zama 'ya'yan Allah
השווה
חקרו Yah 1:12
2
Yah 1:1
Tun fil'azal akwai Kalma, Kalman nan kuwa tare da Allah yake, Kalman nan kuwa Allah ne.
חקרו Yah 1:1
3
Yah 1:5
Haske na haskakawa cikin duhu, duhun kuwa bai rinjaye shi ba.
חקרו Yah 1:5
4
Yah 1:14
Kalman nan kuwa ya zama mutum, ya zauna a cikinmu, yana mai matuƙar alheri da gaskiya. Mun kuma dubi ɗaukakarsa, ɗaukaka ce ta makaɗaicin Ɗa daga wurin Ubansa.
חקרו Yah 1:14
5
Yah 1:3-4
Dukan abubuwa sun kasance ta gare shi ne, ba kuma abin da ya kasance na abubuwan da suka kasance, sai ta game da shi. Shi ne tushen rai, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
חקרו Yah 1:3-4
6
Yah 1:29
Kashegari Yahaya ya tsinkayo Yesu na nufo shi, sai ya ce, “Kun ga, ga Ɗan Rago na Allah, wanda zai ɗauke zunubin duniya!
חקרו Yah 1:29
7
Yah 1:10-11
Dā yana duniya, duniyar ta wurinsa ta kasance, duk da haka duniya ba ta san shi ba. Ya zo ga abin mulkinsa ne, jama'a tasa kuwa ba ta karɓe shi ba.
חקרו Yah 1:10-11
8
Yah 1:9
Akwai hakikanin haske mai shigowa duniya da yake haskaka kowane mutum.
חקרו Yah 1:9
9
Yah 1:17
Domin Shari'a, ta hannun Musa aka ba da ita, alheri da gaskiya kuwa ta wurin Yesu Almasihu suka kasance.
חקרו Yah 1:17
בית
כתבי הקודש
תוכניות
קטעי וידאו