Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa,
yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka.
Ka zama shugaba a kan ’yan’uwanka
bari kuma ’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka.
Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu;
waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”